in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An cimma matsaya game da kafa sabon tsarin mulkin kasar Libya
2016-04-07 10:41:43 cri
Jiya Laraba ne, aka rufe taron shawarwari kan sabon daftarin tsarin mulkin kasar Libya, wanda kwamitin samar da tsarin mulkin kasar ya gudanar a birnin Salalah dake kudancin kasar Oman, inda mahalarta taron suka cimma matsaya guda kan batun tsara daftarin tsarin mulkin kasar tun bayan kawo karshen mulkin Muammar Muhammad Abu Minyar al-Gaddafi a kasar.

Haka kuma, wani mamba a kwamitin ya bayyana wa kafar watsa labarai ta Xinhua cewa, tawagar musamman da MDD ta tura zuwa kasar Libya domin ba da taimako da goyon baya ga kasar, ta jagoranci taron, inda mambobin kwamitin kafa tsarin mulkin kasar Libya su 32 suka halarci taron.,kuma bayan tattaunawar da suka yi tsawon makwanni uku da suka gabata, sun cimma ra'ayi daya kan batutuwan dake shafar sunan kasar, babban birnin kasar, harshen gwamnatin kasar, da kuma matsayin mata a kasar da wasu batutuwan da a da ba a kai ga cimma matsaya guda.

Daga bisani kuma, kwamitin zai kira cikakken zaman taro a birnin Al-bayda dake gabashin kasar Libya a ran 10 ga watan nan da muke ciki, domin kada kuri'u kan daftarin sabon tsarin mulkin kasar.

Kwamitin kafa tsarin mulkin kasar Libya yana da mambobi 55, amma wasu ba su halarci taron ba, sabo da rashin amincewarsu kan wasu ayyukan dake shafar tsara daftarin tsarin mulkin kasar ta Libya.(Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China