in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi kira da kara ba da kariya ga mata a yayin rikice-rikice
2016-03-29 10:42:17 cri
A jiya Litinin, zaunannen wakilin Sin a MDD, Liu Jieyi ya bayyana cewa, kamata ya yi kasashen duniya su kara kiyaye hakki da moriyar mata a yayin rikice-rikice, ta yadda za su kara taka rawar a zo a gani wajen yin rigakafi da daidiata rikice-rikicen.

Kwamitin sulhun MDD ya shirya wani taro mai taken "Amfanin mata wajen yin rigakafi da daidaita rikice-rikicen Afirka", inda Liu Jieyi ya yi jawabin cewa, yanzu ana cikin mawuyacin hali na tabbatar da tsaro a duniya, musamman ma a nahiyar Afirka da yankin Gabas ta Tsakiya da sauransu. Rikice-rikice da barazana sun yi babbar illa ga rayuwar mata.

A sa'i daya, mata sun fara daukar karin nauyi na yin rigakafi da daidaita rikice-rikice a shiyya shiyya.

A sabili da haka, Liu Jieyi ya ce, kamata ya yi kasashen duniya su dauki kwararran matakai, su ba da kariya ga matan dake fama da rikici bisa iyakacin kokari. Sin tana dora muhimmanci kan yin hadin gwiwa da nahiyar Afirka a fannin mata, domin nuna musu goyon baya a fannonin siyasa, tattalin arziki, al'adu, tarbiya, kiwon lafiya da dai sauransu.

Sin na fatan yin aiki tare da sauran kasashen duniya, domin sa kaimi ga samun ci gaban mata a dukkan fannoni.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China