in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hadin gwiwar Sin da Afirka na da makoma mai kyau
2016-03-25 10:04:17 cri
A ranar Laraba 23 ga watan nan ne jakadan kasar Sin dake kasar Afirka ta Kudu Tian Xuejun, ya fidda wani sharhi mai taken "bunkasuwar tattalin arzikin kasar Sin da kyakkyawar makomar hadin gwiwar Sin da Afirka" a jaridar The Star ta Afirka ta Kudu, da ma wasu kafofin watsa labaran kasar.

Cikin sharhin, Mr. Tian ya bayyana cewa, sabbin matakan da kasar Sin ta dauka domin raya tattalin arzikinta, za su tallafa wa hadin gwiwar Sin da Afirka ta Kudu, haka kuma, bai dace a zargin kasar Sin ba, cewar wasu matakan da ta dauka sun haddasa raguwar farashin hajoji a Afirka, da kuma raguwar saurin bunkasuwar tattalin arziki a nahiyar.

Bugu da kari, ya ce, kamar yadda ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya bayyana, babban take na manyan shirye-shirye guda goma na hadin gwiwar Sin da Afirka, shi ne karfafa hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka a fannonin zuba jari, da habaka masana'antu, a maimakon na fannin musayar ciniki, lamarin da ya sa kaimi ga kamfanonin kasar Sin su fara zuba jari a Afirka, yanayin da taimaka wa nahiyar wajen gaggauta bunkasuwar harkokin masana'antu, da kuma kyautata kwarewarsu kan ayyukan dake da nasaba da hakan.

Kaza lika, an fidda wadannan manyan shirye-shirye guda goma a lokacin da ya dace a fuskanci kalubaloli da nahiyar Afirka ke fuskanta a sakamakon sauyin yanayin tattalin arzikin duniya. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China