in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamfanonin Sin da Afirka ta Kudu sun kulla yarjejeniyar hadin gwiwa ta dallar Amurka miliyan 930
2015-11-28 15:50:10 cri
A jiya Jumma'a 27 ga wata, aka yi taron mu'amalar ciniki na kamfanonin Sin da Afirka ta Kudu, watau bikin kulla yarjejeniya a birnin Johannesburg, inda kamfanonin kasashen biyu suka kulla yarjejeniyoyin hadin gwiwa guda 23, da gaba daya jimmilar su ta kai dallar Amurka miliyan 930.

Ma'aikatar kasuwanci ta kasar Sin da ma'aikatar cinikayya da masana'antu ta kasar Afirka ta Kudu sun yi wannan taro na mu'amalar ciniki a tsakanin kamfanonin kasashen biyu, domin ci gaba da habaka mu'amalar harkokin ciniki a tsakanin su da kuma daidaita bunkasuwar cinikin bangarorin biyu, bisa wannan lokacin musamman da za a kira taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka (FOCAC).

Kasar Afirka ta Kudu ita ce babbar abokiyar ciniki ta farko na kasar Sin a nahiyar Afirka, sannan kuma ita ma ta kasance kasa ta farko a Afirka da kasar Sin ta fi fitar da kuma shigar da hajoji.

Yarjejeniyoyin ciniki da kasar Sin da kasar Afirka ta Kudu suka kulla a wannan karo sun shafi fannonin sarrafa karafa, makamashi, likitanci, 'ya'yan itatuwa, abincin teku da dai sauransu. A wajen bikin, kamfanonin Sin 15 suka samu halarta, tare da kamfanoni sama da 50 na kasar Afirka ta Kudu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China