in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na jin dadin ganin kyautatuwar dangantakar dake tsakanin Amurka da Cuba
2016-03-22 11:13:30 cri

A jiya Litinin 21 ga wata, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin madam Hua Chunying ta bayyana a yayin taron maneman labarai cewa, kasar Sin ta lura da cewa, shugaban kasar Amurka Barack Obama ya kai ziyarar aiki a kasar Cuba, inda zai iya ciyar da dangantakar diflomasiyya a tsakanin kasashen biyu gaba. Haka kuma, kasar Sin na jin dadin ganin kasashen biyu suna kokarin maido da dangatakar dake tsakaninsu yadda ya kamata.

Bugu da kari, Hua ta ce, Amurka ta taba kakabawa Cubar takunkumi sama da shekaru 50, amma a halin yanzu, suna kyautata dangantakar dake tsakaninsu cikin himma da kwazo, lamarin da ya dace da moriyar al'ummomin kasashen biyu, tare da kiyaye zaman karko da ci gaban yankin, shi ya sa kasar Sin take fatan Amurka da Cuba za su ci gaba da karfafa mu'amala a tsakaninsu, haka kuma, Sin ta yi kira ga kasar Amurka da ta kawar da takunkumin da take kakabawa Cubar bisa dukkan fannoni ba tare da bata lokaci ba.

Hua ta kara da cewa, a halin yanzu, abin da ya fi muhimmanci cikin harkokin dangantakar kasa da kasa shi ne, yin hadin gwiwa da cimma moriyar juna, kasar Sin da kasar Cuba suna da irin wannan dangantaka mai dogon tarihi, kuma kasar Sin za ta ci gaba da karfafa wannan dangantaka da Cuba a nan gaba ba domin sauran kasashe ba wadda kuma ba za a kawo illa kanta ba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China