in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Faransa za ta karfafa hadin gwiwa da yammacin Afirka domin yaki da ta'addanci
2016-03-16 10:45:36 cri
A jiya Talata 15 ga wata ne ministan harkokin gidan Faransa Bernard Cazeneuve, ya sanar a kasar Kwadebuwa, cewa kasar sa za ta tura dakarun sojin ta na musamman zuwa kasar Burkina Faso, domin aikin karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu wajen yaki da ta'addanci.

A jiyan ne dai ministan harkokin wajen kasar Jean-Marc Ayrault, da na harkokin gidan kasar Bernard Cazeneuve, suka isa birnin Abidjan fadar mulkin kasar Kwadebuwa, inda suka gana da shugaban kasar Alassane Ouattara, sa'an nan, suka ziyarci garin Grand Bassam dake kudancin kasar, inda dakarun sa kai suka kai hari ga masu yawon shakatawa a kwanakin baya, domin gabatar da ta'aziyar wadanda suka rasu sakamakon harin, ciki kuma har da 'yan kasar Faransa su hudu.

Haka kuma, a yayin ziyararsa a kasar, minista Cazeneuve ya sanar da cewa, kasar Faransa za ta tura sojojin rundunar musamman zuwa Ouagadougo fadar mulkin Burkina Faso, domin ba da shawara, da taimako yadda ya kamata, da kuma gaggauta gudanar da matakan dakile ayyukan ta'addanci, da dai sauran kalubalolin masu alaka da hakan a yankin yammacin Afirka. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China