in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Faransa za ta kara tsawaita wa'adin dokar ta baci zuwa watanni 3
2016-01-23 13:34:19 cri
A ranar 22 ga wata da dare, fadar shugaban kasar Faransa ta bayar da sanarwa cewa, shugaba François Hollande ya yi bayani a wannan rana, inda ya ce, gwamnatinsa za ta duba wani daftarin doka a yayin taron majalisar ministoci da za a gudana a ranar 3 ga wata mai zuwa, da nufin kara tsawaita wa'adin dokar ta baci zuwa watanni 3.

Sanarwar ta ce, shugaba Hollande da firaminista Manuel Valls sun gana da wakilan jam'iyyun siyasa dake da kujeru a majalisar dokoki, domin neman ra'ayi kan wani shirin kuduri na gyara tsarin mulki dake da nufin tabbatar da tsaron kasar.

An tayar da jerin ayyukan ta'addanci a ranar 13 ga watan Nuwanban bara a birnin Paris na Faransa, wadanda suka hadddasa rasuwar mutane a kalla 130, yayin da 350 suka jikata, wadanda kuma kungiyar IS ta dauki alhakin kaiwa. A ranar 14 ga watan Nuwanban da ya gabata, fadar shugaban kasar ta sanar da shiga dokar ta baci na kwanaki 12. A ranar 26 ga watan din, ta kara tsawaita wa'adin dokar ta baci zuwa ranar 26 ga watan Faburairu na bana. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China