in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wang Yi: An nuna goyon baya ga kamfanonin Sin da su samu bunkasuwa a ketare
2016-03-07 20:44:18 cri
A yau Litinin 7 ga wata, ministan harkokin waje na Sin, Wang Yi ya bayyana cewa, ma'aikatar harkokin waje ta Sin na goyon bayan bunkasar kamfanonin Sin dake ketare.

A wannan rana ne dai aka gudanar da taron wakilan al'ummar lardin Zhejiang mahalarta taron shekara shekara na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin, domin nazartar daftarin shirin bunkasa tattalin arziki da zaman al'umma na shekaru biyar biyar a karo na 13. Mista Wang Yi da ya zo sauraron muhawarar ya bayyana cewa, Afirka ta zama muhimmiyar nahiya wajen hadin gwiwa da Sin, musamman ma a fannin masana'antu. Kasashen Afirka su ma sun gano cewa, bai kamata su nemi samun bunkasuwa bisa albarkatunsu kadai ba, wato dole ne su kara saurin kafa masana'antu, da raya tattalin arzikinsu ta hanyoyi daban daban. A sabili da haka, hanyar da Sin ke bi ta yin hadin gwiwa ta yi matukar dacewa da bukatunsu. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China