in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sabunta: An bude taron cikakken zama na 4 na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin
2016-03-05 17:20:33 cri
A safiyar Asabar din nan 5 ga wata ne, aka bude taron shekara-shekara karo na 4 na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin wato NPC na 12.

A yayin bikin, firaministan gwamnatin kasar Sin Li Keqiang ya gabatar da wani rahoto game da ayyukan da gwamnatinsa ta yi a shekarar 2015, da ayyukan da gwamnatin za ta yi a shekarar 2016. A cikin rahoton, Li Keqiang ya nuna cewa, idan ana son samun kyakkyawar makoma, dole ne a yi namijin kokarin yin aiki. Dole ne duk al'ummomin kasar su dunkule waje daya a karkashin jagorancin kwamitin tsakiyar jam'iyyar JKS wadda ke karkashin shugancin babban sakatare Xi Jinping, ta yadda za a iya dukufa ka'in da na'in wajen ciyar da kasar Sin gaba domin kokarin cimma babban burin farfadowar al'ummomin kasar.

Wakilai kusan dubu 3, ciki har da shugaban kasar Xi Jinping da wasu shugabannin kasar suka halarci taron. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China