in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban sakataren MDD ya kai ziyara a kasar Sudan ta Kudu
2016-02-27 13:29:32 cri
A ranar Alhamis din makon nan, babban sakataren MDD, Ban Ki-moon ya isa birnin Juba, hedkwatar kasar Sudan ta Kudu, domin yin shawarwari da shugaban kasar, Salva Kiir. A yayin ganawarsu, shugaba Kiir ya yi alkawari ga mista Ban cewa, zai gudanar da yarjejeniyar daidaita rikicin Sudan ta Kudu yadda ya kamata.

Ministan harkokin waje da yin hadin gwiwa da sauran kasashen duniya na Sudan ta Kudu, Barnaba Marial Benjamin ya bayyana cewa, ziyarar magatakardan MDD na da muhimmanci kwarai ga kasar Sudan ta Kudu da jama'arta. Makasudin ziyararsa shi ne kalubalantar bangarori daban daban da su gudanar da yarjejeniyar yadda ya kamata.

Bayan haka, mista Benjamin ya bayyana cewa, mista Ban yana kokarin lallashin shugaban jam'iyyar adawa, Riek Machar da ya dawo birnin Juba tun da wuri, ta yadda za a iya kafa hadaddiyar gwamnatin rikon kwarya lami lafiya.

An ba da labarin cewa, Ban Ki-moon zai yi shawarwari da tawagar musamman ta MDD kan batun Sudan ta Kudu, da wasu jami'an wurin, da kuma wasu sarakunan gargajiya, domin sauraron ra'ayoyinsu, da rarraba musu ra'ayinsa. Daga bisani, Ban Ki-moon zai ci gaba da kai ziyararsa a kasar Kongo Kinshasa, domin yin bincike kan yanayin da ake ciki a fannin jin kai.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China