in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Sudan ya bayar da umarnin bude kan iyakar kasarsa da Sudan ta kudu
2016-01-28 10:17:25 cri

Shugaban Omar al-Bashir na Sudan ya ba da umarnin sake bude kan iyakar kasar da makwabciyarsa Sudan ta kudu.

Kamfanin dillancin labaran kasar SUNA ya ruwaito shugaba al-Bshir na umartar dukkan hukumomin da abin ya shafa, da su dauki dukkan matakan da suka wajaba na ganin sun aiwatar da wannan umarni.

A ranar Talata ce shugaban Salva Kiir Mayardit na Sudan ta kudu,ya umarni rundunonin sojojin kasar, da su ma su janye daga wuraren da suka ja daga a kan iyakar Sudan. Ya ce kamata ya yi dakarun su janye da a kalla tazarar mil 5 kudu daga kan iyakar da aka shata a ranar 1 ga watan Janairun shekarar 1956, kamar yadda aka cimma a yarjejeniyar zaman lafiya ta 2005.

A watan Yunin shekarar 2011 ne kasar Sudan ta rufe kan iyakarta da Sudan ta kudu, sakamakon barin wutar da mayakan 'yan tawayen SPLM bangaren arewaci suka kaddamar a yankin Darfur na Sudan ta kudu.

Sudan dai na zargin makwabciyar Sudan ta kudu ta baiwa 'yan tawayen mafaka da taimakon kudi da nufin tayar da zaune tsaye a kan iyakarta.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China