in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawagar sojojin kiyaye zaman lafiya rukuni na biyar ta Sin za ta tashi zuwa Sudan ta Kudu
2015-12-25 20:03:10 cri
A yau Jumma'a 25 ga wata, aka yi bikin tashin tawagar sojojin kiyaye zaman lafiya rukuni na biyar da kasar Sin za ta tura zuwa kasar Sudan ta Kudu a ma'aikatar kiyaye zaman lafiyar jama'a ta kasar Sin. Tawagar dake kunshe da sojoji guda 13 za ta tashi zuwa kasar Sudan ta Kudu domin gudanar da ayyukan kiyaye zaman lafiya a kasar na tsawon shekara daya.

Kafin tashinsu kuma, an ba sojojin tawagar horo na tsawo watanni biyu domin kara kwarewarsu kan ayyukan kiyaye zaman lafiya, ba da agaji, harba bindigogi da kuma jin harshen Turanci da dai sauransu, haka kuma dukkansu sun saurari jawabin da MDD ta yi musu.

Bisa labarin da aka samu, an ce, tun daga shekarar 2000, ya zuwa yanzu, gaba daya ma'aikatar kiyaye zaman lafiyar jama'a ta kasar Sin ta taba aike da sojojin kiyaye zaman lafiya guda 2305 zuwa yankuna guda 9 da abin ya shafa, da suka hada da East Timor, Bosnia da Herzegovina, Liberia, Sudan da kuma Sudan ta kudu da dai sauran yankunan na kasashen duniya da abin ya shafa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China