in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyoyin da suke adawa da gwamnatin Syria sun amince da yarjejeniyar tsagaita bude wuta
2016-02-25 13:37:46 cri
Babban kwamitin shawarwari na kungiyoyin dake adawa da gwamnatin kasar Syria ya sanar a Larabar da ta gabata cewa, ya amince da yarjejeniyar tsagaita bude wuta, wanda Amurka da Rasha suka tsara a kwanan baya, bisa yarjejeniyar za'a tsagaita bude wuta na tsawon makoni biyu.

Haka kuma, kwamitin yana ganin cewa tsagaita bude wutar na makonni biyu zai taimakawa kungiyoyinsu wajen bincike game da yadda gwamnatin kasar ke gudanar da yarjejeniyar.

Ma'aikatar harkokin wajen Syria ta sanar a ranar Talatar da ta gabata cewa, gwamnatin kasar ta amince da yarjejeniyar tsagaita bude wuta, amma ba za ta dakatar da matakan soja da ta ke dauka kan kungiyoyin IS da al-Qaeda dake kasar ba.

Bugu da kari ta sanar da cewar, kasar za ta tattauna da Rasha wajen tabbatar da wadanne yankuna da kungiyoyi ne dake kunshi cikin yarjejeniyar, domin aiwatar da yarjejeniyar cikin lokaci kuma yadda ya kamata. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China