in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhun MDD ya yi kira ga kungiyoyi daban daban na Syria da su hanzarta gudanar da shawarwarin zaman lafiya
2016-02-24 11:12:26 cri
Kwamitin sulhun MDD ya gabatar da sanarwa a jiya Talata, inda ya yi Allah wadai da harin bama-baman da aka kai kwanakin baya a birnin Damascus da wasu sassa a kasar Syria, kana ya yi kira ga kungiyoyi daban daban na kasar Syria da su hanzarta komawa ga teburin shawarwari domin samar da zaman lafiya karkashin sa-idon MDD.

Sanarwar kwamitin sulhun ta kuma nuna goyon baya ga kokarin da manzon musaman na babban sakataren MDD mai kula da batun Syria Staffan de Mistura ya yi, kana ya jadadda bukatar aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma a taron ministocin harkokin waje karo na 4 na kasashen da ke goyon bayan Syria da kuma kudurorin da kwamitin sulhun ya tsaida da sauransu.

Bugu da kari, kwamitin sulhun ya yi kira ga kungiyoyi daban daban na kasar Syria da su baiwa hukumomin jin kai damar kaiwa ga 'yan kasar Syria da ke matukar bukatar agaji, musamman ga jama'ar da ke yankunan da rikice-rikice ya rutsa da su

A ranar 3 ga watan 25 ga watan Fabrairu ne ake saran gudanar da sabon zagayen tattaunawar zaman lafiya game da kasar ta Syria da aka dakatar a ranar 3 ga watan Fabarairu a birnin Geneva. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China