in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ma'aikatar harkokin wajen Sin ta yi bayani kan batun Nanhai
2016-02-23 11:06:45 cri
Kwanan baya, Amurka tana zargin kasar Sin cewa, kasar ta mai da harkokin tekun Nanhai a matsayin harkar soja, dangane da wannan lamarin, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta bayyana a ranar litinin din nan cewar, kasar Amurka ce ta sanya kasar Sin ta gibge makamai masu linzami a yankin sabo da Amurka ta kan kai jiragen sama na sojojin tekunta zuwa yankin domin yin bincike.

Hua ta kara da cewa, kwanan bayan, kasar Amurka ta sha zargin kasar Sin wajen mai da harkokin tekun Nanhai a matsayin harkar soja, amma a hakika dai, kasar Amurka ba ta fadi gaskiya ba.

Hua ta ce, kasar Sin tana gudanar da aikin kiyaye tsaron kasa a yankin Nanhai yadda ya kamata, kaman irin aikin da kasar Amurka ta yi a Hawaii.

Bugu da kari, ta nuna cewa, jiragen sama na sojojin tekun kasar Amurka su kan yin bincike a yankin, lamarin yana kuma ci gaba da karuwa cikin shekaru baya bayan nan, wannan shi ne dalilin da ya haddasa tabarbarewar yanayin tsaro a yankin Nanhai, muna fatan kasar Amurka ta dakatar da yi wa kasar Sin iri wannan zargi na bai dace ba, haka kuma, ta tsayar da matakan da ta dauka a wannan yanki, kada a haddasa karin barazana ga yanayin tsaro, kaza lika, ta kuma cewa, muna fatan kasar Amurka za ta iya ba da gudummawa wajen kiyaye zaman lafiya da zaman karko a yankin yadda ya kamata. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China