in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Kamaru sun harbe 'yan kungiyar Boko Haram 162
2016-02-16 20:58:02 cri
Ministan watsa labaru na kasar Kamaru, Issa Tchiroma Bakary ya shelanta cewa, daga ranar 11 zuwa 14 ga wata, sojojin kasar sun harbe 'yan kungiyar Boko Haram 162, tare da lalata cibiyoyin samar da makamai da kuma makamansu da dama. Dadin dadawa, sojojin sun kwace garin Goshi dake arewa maso gabashin Najeriya daga hannu mayakan kungiyar. Yanzu haka garin yana hannun sojojin Najeriya.

Mista Bakary ya furta cewa, sojojin Kamaru sun ceto mutane kimanin 100 da 'yan kungiyar Boko Haram suka yi garkuwa da su.

Bugu da kari,minisan ya ce, an gudanar da wannan aiki ne tare da hadin gwiwar Nijeriya. Kuma sojojin Kamaru biyu sun rasu a lokacin wannan fafatawa.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China