in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Zuma ya yaba da yarjejeniyar sauyin yanayi da aka cimma
2015-12-14 09:42:12 cri
Shugaba Jacob Zuma a kasar Afirka ta kudu ya bayyana yarjejeniyar sauyin yanayi da aka cimma a taron Paris a matsayin wani gagarumin ci gaba a kokarin da ake yi na ganin dukkan kasashen duniya sun tashi tsaye a yakin da ake kan matsalar sauyin yanayin duniya.

Shugaba Zuma ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da fadar shugaban kasar ta fitar a birnin Pretoria, inda ya yi fatan yarjejeniyar za ta taimaka wajen samar da makoma mai kyau ta hanyar magance matsalar sauyin yanayi baki dayan ta.

Zuma ya ce, baki dayan kan kungiyar G77 da kasar Sin wadda kasar ta Afirta ta kudu ke jagoranta a hade yake a taron na Paris, inda suka gabatar da bukatunsu da suke fatan ganin an amince da shi cikin murya guda.

A ranar Asabar ne aka kai ga cimma yarjejeniya ta karshe a taron sauyin yanayi na duniya da MDD ta shirya a birnin Paris na kasar Faransa, inda ake fatan kasashen duniya za su rage yawan iskar da ke dumama yanayin duniya da suke fitarwa nan da shekara 2020.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China