in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Afirka ta Kudu ta lashi takwabin kawar da cutar AIDS a kasar
2015-11-30 09:46:07 cri

Mataimakin shugaban kasar Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa ya bayyana kudurin gwamnatin kasarsa na ganin ta samar da al'ummar da ba cutar AIDS a cikinta.

Mr Ramaphosa wanda ya bayyana hakan cikin wata sanarwa gabanin bikin ranar yaki da cutar AIDS na duniya da zai gudana a ranar 1 ga watan Disamba, ya bayyana cewa, sun dauki matakai da dama na ganin an kawar da cutar ta AIDS kwata-kwata a tsakanin al'umma.

Don haka,ya yi kira ga daukacin 'yan kasar Afirka ta Kudu da su daura damarar ganin an kawar da cutar a cikin kasar da ma duniya baki daya.

Bayanai na nuna cewa, masu dauke da cutar AIDS sama da miliyan 3 ne a kasar Afirta ta Kudu ke amfani da maganin rage kaifin cutar baya ga kasancewarta kasar da ke kan gaba wajen shirye-shiryen yaki da cutar AIDS a duniya.

Baya ga matsalolin da masu fama da cutar ta AIDS ke fuskanta a kasar, ita ma kasar tana fama da kalubaloli da dama, gami da karuwar sabbin masu kamuwa da cutar da ake samu, musamman tsakanin mata da matasa.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China