in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta bayyana ra'ayinta kan harbar tauraron dan Adam da Koriya ta Arewa ta yi
2016-02-07 16:16:51 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta bayyana a yau Lahadi 7 ga wata cewa, game da harbar tauraron dan Adam da kasar Koriya ta Arewa ta yi, inda kasar Sin ta bayyana fatanta na ganin bangarorin da abin ya shafa sun kai zuciya nesa, a yayin da ake daukar matakai yadda ya kamata, domin kaucewa tabarbarewar yanayin a yankin Koriya da kuma kiyaye zaman karko a yankin.

Kasar Sin ta gano Koriya ta Arewa ta harba wani tauraron dan Adam, kuma tana sanya ido kan ra'ayoyi na bangarorin da abin ya shafa.

Haka kuma, kasar na ganin cewa, ko da yake, Koriya ta Arewa tana da ikon yin amfani da sararin samaniya cikin lumana, amma a halin yanzu, ana hana ta aiwatar da ikonta game da wannan batu bisa tsarin kwamitin sulhu na MDD, shi ya sa, kasar Sin ta bayyana bakin cikinta bisa matakin da Koriya ta Arewa ta dauka na sabawa gamayyar kasa da kasa, domin harba tauraron dan Adam da fasahar makamai mai linzami.

Bugu da kari, ta ce, kullum kasar Sin na ganin cewa, za a iya shimfida zaman karko da zaman lafiya na dindindin a yankin Koriya ta hanyar yin shawarwari. Shi ya sa, ya kamata bangarorin da abin ya shafa su fara yin shawarwari a tsakaninsu tun da wuri, domin kaucewa tabarbarewar yanayi a wanan yankin. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China