in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Koriya ta Kudu ta yi suka a kan kaddamar da roka da Koriya ta arewa ta yi
2016-02-07 12:32:28 cri
Shugabar kasar Koriya ta Kudu, Park Geun-hye a yau din nan Lahadi ta yi suka a kan kaddamar da rokan da kasar Koriya ta arewa ta yi, tana mai bayyana shi matakin tsokana ne da ba za'a amince da shi ba.

Kamar yadda sanarwar da ofishinta ya fitar an yi ganawar gaggawa bayan da makwabciyar ta Koriya ta Arewa ta kaddamar da roka misalin karfe tara da rabi na safiyar wannan rana daga tashar rokarta a Tongchanr-ri dake gabar yamma.

Madam Park ta ce kasar Koriya ta arewar ta inganta fasahar makamanta na linzami domin dalili daya kawai na ci gaba da mulkinta, tana mai kiran wannan kaddamarwar a wani kalubale ga kasashen duniya ganin yadda aka yi shi lokacin da kwamitin tsaron MDD ke cikin tattaunawar yuwuwar samar da sabbin takunkumi a kan kasar dangane da gwajin makaman Nukiliya da ta yi karo na 4. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China