in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamata ya yi bangarorin da batun nukiliya a zirin Koriya ya shafa su yi kokarin kauracewa tsanantar yanayi
2016-01-11 21:44:26 cri
A yau Litinin 11 ga wata ne kakakin ma'aikatar harkokin waje ta Sin mista Hong Lei, ya bayyana cewa tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a arewa maso gabashin nahiyar Asiya, ya dace da moriyar bangarori daban daban. Don haka Sin ke fatan bangarorin da abin ya shafa za su kai zuciya nesa, su kuma dauki matakai cikin taka-tsamtsam, domin kaucewa tsanantar yanayi a kai a kai.

Mista Hong ya fadi haka ne a gun taron manema labaru da aka shirya a wannan rana, yayin da yake mai da martani ga batun shigowar wani jirgin saman yakin mallakar Amurka samfuri B-52 cikin zirin Koriya.

A daya bangaren kuma an labarta cewa, rundunar sojan Koriya ta Kudu ta farfado da yayata farfaganda da take gudanarwa da amsa kuwa kan kasar Koriya ta Arewa a kan iyakar kasashen biyu.

Game da wannan batu, Mr. Hong ya bayyana cewa, Sin na tsayawa tsayin daka wajen ba da kariya ga tsarin hana bazuwar makaman nukiliya a duniya, da rashin yarda da gwajin nukiliya da kasar Koriya ta Arewa ke yi. Kaza lika kasar ta Sin na fatan yin mu'amala da bangarori daban daban, a kokarin ta na sa kaimi ga farfado da shawarwari tsakanin su game da batun nukiliya a zirin Koriya, ta yadda za a cimma burin kawar da makaman nukiliya a zirin, tare da kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a arewa maso gabashin nahiyar Asiya cikin hanzari.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China