in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na fatan bangarorin da batun Syria ya shafa sun dawo teburin shawarwari
2016-02-01 20:15:07 cri
A ran 29 ga wata ne, manzon musamman na babban magatakardan MDD dake kula da batun Syria Staffan de Mistura ya gana da tawagar gwamnatin kasar Syria a birnin Geneva na kasar Switzerland, lamarin da ya nuna bude wani sabon zagaye na shawarwarin neman sulhu a tsakanin bangarori daban daban na kasar Syria, inda ake sa ran kwashe watanni 6 ana tattaunawa

Dangane hakan, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasa ta Sin Lu Kang ya bayyana a yau Litinin cewa, yin shawarwarin neman sulhu ita ce hanya kacal da za a iya warware batun Syria da kuma samun sakamako mai gamsarwa.

Kaza lika, ya ce, ya kamata bangarorin biyu da rikicin kasar ya shafa su karfafa fahimtar juna a tsakaninsu, ta yadda za a cimma nasarar shawarwarin, sa'an nan kuma, ya kamata gamayyar kasa da kasa, musamman ma kasashen dake yankin su taimaka yadda ya kamata. Kasar Sin ita ma za ta ci gaba da yin hadin gwiwa da bangarorin da abin ya shafa domin ciyar da aikin warware matsalar Syria ta hanyar siyasa gaba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China