in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta bukaci a kara hadin gwiwwa wajen yaki da ta'addanci
2015-12-17 09:24:54 cri
Akwai bukatar kasashen Afrika su kara hada hannu domin yakar ta'addanci wanda ya rage daya daga cikin manyan kalubalolin da nahiyar ke fuskanta, in ji kwamishinan zaman lafiya da tsaro na Kungiyar tarayyar kasashen Afrika AU, Smail Chergui jiyar Laraba 16 ga wata.

Ta'addanci da tashin hankali na masu tsattsauran ra'ayi ya rage daya daga cikin damuwar kungiyar, kuma kasashen Afrika in ji shi, dole su inganta kokarin da suke yi na dakile wannan matsala tare da magance duk wani dalilin da ke taimaka masu bazuwa.

Mr. Smail Chergui a cikin jawabin da ya yi wajen bude taron shekara shekara karo na 9 na cibiyar bincike da nazari kan ta'addanci na Afrika, ya ce kungiyar AU da cibiyar suna ci gaba da taimaka ma mambobi kasashe a nasu kokarin na ganin an hana kungiyoyin 'yan ta'adda samun sabbin dabaru da kuma kudin tafiyar da ayyukansu.

A cewar kwamishinan zaman lafiya da tsaro na kungiyar AUn, yanayin tsaro a nahiyar yana tabarbarewa, sannan ana fuskantar barazanar ta'addanci da kungiyar 'yan ta'adda dake da alaka da DAESH, yana mai bayanin cewa dakile ta'addanci ya rage babban kalubale dake fuskantar nahiyar. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China