in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi Allah wadai da harin da kungiyar Al-Shabaab ta kai kan sansanin soja na AU
2016-01-16 13:22:57 cri
A jiya Jumma'a 16 ga wata, babban magatakardan MDD Ban Ki-moon, da kwamitin sulhun MDD sun ba da sanarwar yin Allah wadai da harin da kungiyar Al-Shabaab ta kai kan wani sansanin soja na kungiyar tarayyar kasashen Afirka (AU) a wannan rana.

A cikin sanarwarsa, Ban Ki-moon ya jaddada cewa, harin ba zai rage kwarin gwiwar yin hadin gwiwa tsakanin MDD da kungiyar AU da tawagar musamman ta AU kan batun Somaliya ba a kokarinsu na nuna goyon baya ga jama'a da gwamnatin kasar Somaliya.

A nasa bangare, kwamitin sulhun MDD ya yi Allah wadai da wannan danyen aiki da babbar murya a cikin sanarwarsa, kuma ya nuna goyon bayansa ga tawagar musamman ta AU kan batun Somaliya a kokarinta na yaki da ta'addanci da barazanar kungiyoyi masu dauke da makamai a Somaliya.

Kungiyar Al-Shabaab ta kai hari kan wani sansanin soja na kungiyar AU dake yankin Gedo na kudancin Somaliya a jiya, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar sojojin kungiyar AU da dama.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China