in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen kasar Sin ya yi bayani kan ziyarar shugaba Xi a Saudiya, Masar, Iran da kuma hedkwatar kungiyar AL
2016-01-24 14:44:47 cri
Daga ranar 19 zuwa ta 23 ga watan Janairun bana, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kai ziyara a kasashen Saudiya, Masar, Iran, da kuma hedkwatar kungiyar kasashen Larabawa (AL). Yayin kammala wannan ziyara, ministan harkokin waje na Sin mista Wang Yi ya yi bayani ga manema labrai kan ziyarar.

Mr. Wang ya ce, a farkon wannan shekarar, shugaba Xi Jinping ya kai ziyara a kasashen Saudiya, da Masar, da kuma Iran ne, domin kaddamar da muhimmin aikin diplomasiyya na farko a bana. Wadannan kasashe uku suna da babban tasiri a yankin Gabas ta Tsakiya. Akwai dankon zumunci tsakaninsu da Sin, haka kuma suna gudanar da hadin gwiwa da kasar Sin a fannoni daban daban. Sau da yawa shugabannin kasashen uku sun gayyaci shugaba Xi domin kai ziyara a kasashensu. A wannan karo, shugaba Xi ya karbi goron gayyatar tare da mai da ziyara a matsayin ziyara ta farko da ya kai ketare a bana. Wannan ya bayyana muhimmancin da Sin ta dora kan bunkasa dangantaka tsakaninta da wadannan kasashen uku, har ma da yankin Gabas ta Tsakiya.

A yayin ziyararsa, shugaba Xi ya kai ziyara a birane hudu cikin kwanaki biyar, inda ya halarci ayyuka sama da 40, tare da yin shawarwari da shugabannin kasashen uku da shugabannin kungiyoyin shiyya shiyya guda uku. Baki daya, an rattaba hannu kan yarjeniyoyin hadin gwiwa 52 a yayin wannan ziyara. Ziyarar shugaba Xi a yankin Gabas ta Tsakiya a wannan karo, ta sami babbar nasara, inda aka cimma burin sada dankon zumunci, da yin hadin gwiwa da samun moriyar juna, da sa kaimi ga tabbatar da zaman lafiya da fahimtar juna a wannan yanki, da kuma sa kaimi ga samun ci gaba da zaman lafiya a kasa da kasa baki daya.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China