in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin da takwaransa na Masar sun halarci bikin raya murnar cika shekaru 60 da kulla dangantakar kasashen biyu
2016-01-22 09:13:12 cri

Shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na kasar Masar Abdul Fatah Al-Sisi, sun halarci bikin murnar cika shekaru 60 da kulla dangantaka tsakanin kasashen biyu, kuma an gudanar da bikin nuna al'adu na wannan shekarar na kasashen biyu a ranar 21 ga wannan wata a wajen ibada na Luxor da ke kasar ta Masar.

Bayan da shugabannin kasashen biyu suka shiga wurin ibada, sun tofa albarkacin bakinsu game da daddaden tarihi da al'adun kasashen biyu, kuma sun waiwayi mu'amalar kasashen biyu. Shugaban Xi ya yi nuni da cewa, kasashen Sin da Masar suna da dadadden tarihi, ya zama wajibi kasashen biyu su inganta mu'amalar al'adu da zurfafa sada zumunta a tsakanin jama'a, don karfafa bangarorin biyu domin su samu bunkasuwa da wadata.

Shugaban Al-Sisi na Masar ya bayyana halartar bikin da shugaban Xi yayi da cewa, kasar Sin na nuna goyon baya ga Masar. Sannan ya bukaci kasashen biyu su inganta musayar al'adu, don ci gaba da zama aminan juna.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China