in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya bayar da sharhi a jaridar kasar Masar
2016-01-20 10:43:16 cri
A jiya Talata 19 ga wata, a yayin da shugaban kasar Sin Xi Jinping yake shirin kai ziyara a kasar Masar, jaridar Al Ahram ta kasar Masar ta wallafa sharhin da ya gabatar, mai taken "Ciyar da zumunta a tsakanin Sin da kasashen Larabawa gaba".

A cikin sharhin, Mr. Xi ya ce bisa gayyatar da shugaban kasar Masar Abdel-Fattah al-Sisi ya yi masa, zai kai ziyara a kasar Masar. Kuma wannan ne karo na farko da ya kai ziyara a kasashen dake yankin gabas ta tsakiya da kasashen Larabawa, bayan da ya hau kujerar shugabancin kasar Sin. Kana shi ne karo na farko da ya kai ziyara a kasashen waje a shekarar 2016.

A cewar shugaban, kasar Masar ita ce kasa ta farko da ta kulla dangantakar diplomasiyya a tsakaninta da kasar Sin a cikin kasashen Larabawa, don haka dangantakar dake tsakanin sassan biyu ta zamo mafari na raya dangantakar dake tsakanin Sin da kasashen Larabawa, kana ta wakilci dangantakar dake tsakanin Sin da kasashen Larabawa.

Shugaban kasar Sin ya kara da cewa, fadin kasar Sin da kasashen Larabawa ya kai kashi daya cikin shida bisa jimillar fadin dukkan yankunan duniya, kuma yawan jama'arsu ya kai kashi daya cikin hudu bisa daukacin adadin mutanen duniya, kuma ko shakka babu akwai kyakkyawar makoma game da hadin gwiwar bangarorin 2.

Shugaban kasar Sin ya ce a nan gaba, bangarorin biyu za su ci gaba da raya hadin gwiwarsu a dukkan fannoni, da kuma dangantakar dake tsakaninsu, da sada zumunta, don amfanin jama'ar bangarorin biyu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China