in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jakadan Sin dake Masar: ziyarar shugaba Xi Jinping za ta sa kaimi ga raya dangantaka tsakanin Sin da Masar a dukkan fannoni
2016-01-18 11:24:40 cri
Ana sa ran cewa, shugaban kasar Sin Xi Jinping zai gudanar da ziyarar aiki a kasar Masar a 'yan kwanaki masu zuwa, a wani mataki na raya hadin gwiwa da fadada zumunta tsakanin Sin da kasar ta Masar.

Game da hakan, jakadan Sin dake kasar Masar Song Aiguo, ya bayyawa wakilinmu a jiya Lahadi 17 ga wata cewa, a halin yanzu ana karfafa hadin kai da zumunta tsakanin sassan biyu, kuma ziyarar ta shugaba Xi Jinping a Masar, za ta sa kaimi ga inganta hadin gwiwar kasashen a fannonin siyasa, da tattalin arziki, da al'adu, da ilmi, da yawon shakarawa da dai sauransu. Ya ce ta hakan za a bunkasa hadin gwiwarsu, da raya dangantakar abokantakar kasashen biyu daga dukkan fannoni. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China