in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu na MDD ya yi zargi kan harin boma-boman da aka kai a hedkwatar Somaliya
2013-11-10 16:13:56 cri
A ranar Asabar 9 ga wata, kwamitin sulhu na MDD ya ba da sanarwar yin Allah wadai da harin boma-boman da aka kai wa birnin Mogadishu, hedkwatar kasar Somaliya, tare da nuna goyon bayansa ga kokarin tabbatar da zaman lafiya da samun daidaito a cikin wannan kasa.

A ran 8 ga wata, kungiyar Al-Shabaab ta kasar Somaliya ta kai harin boma-bomai da aka dasa cikin mota a birnin Mogadishu, hedkwatar kasar, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama, yayin da wasu suka jikkata. Kwamitin sulhu na MDD ya nuna goyon baya ga kasashen duniya da mahukuntan kasar Somaliya wajen kawar da barazanar kungiyar kishin islama ta Al-Shabaab.

Dadin dadawa, kwamitin sulhu na MDD ya nanata cewa, ko wane irin ta'addanci na kasancewa tamkar barazana mai tsanani ga zaman lafiya da tsaron duniya. Harin ta'addancin da duk wanda ya kai bisa ko wane irin dalili a ko ina kuma ko yaushe, laifi ne ke nan, kuma ya zama tilas a gurfanar da shi a gaban kotu.

A sabili da haka, kwamitin sulhu na MDD ya yi aniyar yaki da ko wane irin ta'addanci bisa kundin tsarin mulkin MDD.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China