in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Aljeriya: Taron ministoci ya amince da shirin yi wa kundin tsarin mulkin kasa gyaran fuska
2016-01-12 10:22:32 cri

Shugaban kasar Aljeriya Abdelaziz Bouteflika ya jagoranci a ranar Litinin a birnin Alger wani taron ministoci wanda a karshe ya amince da shirin kawo gyaran fuska ga kundin tsarin mulki.

Matakin farko na wannan shirin kawo gyara, shugaban kasa ya amince da shi a karshen watan Disamba kana darektan fadar shugaban kasa Ahmed Ouyahia ya gabatar a ranar Talata, na kunshe da wasu muhimman matakai, kamar amincewa da harshen Tamazight a matsayin harshen aiki da kuma tsai da zuwa biyu adadin wa'adin shugaban kasa na shekaru biyar.

Yanzu matakin karshe na wannan muhimmin kundin doka ya samu amincewa, kuma za a gabatar da shi a gaban majalisun kasar biyu, da kwamitin kasa da kuma yiwuwar isar da shi ga zaben raba gardama. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China