in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Aljeriya ta dauki niyyar yin tsimi ba tare da tsuke bakin aljihu ba
2015-07-05 13:42:27 cri
Faraministan kasar Aljeriya Abdelmalek Sellal ya tabbatar a ranar Asabar a birnin Alger cewa kasarsa ta shiga cikin wani shirin yin tsimi ta hanyar rage kashe kashen kudin gwamnati ba cikin tsuke bakin aljihu ba.

Manufar gwamnatin ita ce takaita kashe kashen kudin gwamnati. Amma wannan manufa ba wai tana nufin tsuke bakin aljihu ba, in ji mista Sellal a yayin wata ziyarar aiki da ya kai a Wilaya da ke karkarar birnin Alger, tare da nuna cewa faduwar farashin man fetur wata dama ce domin canja siyasar tattalin arzikin kasar bisa manufar fita da yin dogaro da man fetur da kuma kafa wasu hanyoyin samun arziki da ayyukan yi.

Bayan jerin faduwar farashin danyen mai, wanda kudaden fitar da man fetur ke wakiltar kashi 95 cikin 100 na kudin shigar da kasar take samu, gwamnatin Aljeriya ta sanar da daukar matakai, wanda suka hada da soke sabbin ma'aikatun dake lakume kudi a cikin harkokin gwamnati da kuma dakatar da wasu ayyukan gine ginen ababen more rayuwa. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China