in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Aljeriya na fargabar ganin cewa rikicin Libiya ya tura shiyyar cikin rashin tsaro
2015-08-17 11:27:38 cri
Kasar Aljeriya ta bayyana dumuwarta a ranar Lahadi game da abin da take kira tashin hankalin Libiya na tsoron ganin ya tura shiyyar cikin rashin tsaro tare da jaddada kiranta na ganin an kafa wata gwamnatin hadaka a Libiya cikin gaggawa, a cikin wata sanarwa da ma'aikatar harkokin wajen kasar Aljeriya ta fitar, tare da yin alla wadai da babbar murya kan ayyukan ta'addanci na baya bayan nan a Syrte da ke arewacin Libiya.

Amma duk da wanna matsala, ma'aikatar harkokin wajen Aljeriya ta yi tsaya imanin cewa, 'yan kasar Libiya dake gaba da juna za su iya fuskantar kalubalen tsaro da kuma kai ga kiyaye zaman jituwa na 'yan kasar, fadin kasar Libiya, da 'yancin kasar Libiya da kuma hada kan al'ummomin Libiya baki daya.

Bisa wannan manufa, Aljeriya ta jaddada niyyarta na yin aiki tare da dukkan bangarorin Libiya, da ma kungiyoyin ta'addanci da MDD ta amince da su cikin shirin warware rikicin da kasar take fama da shi tun yau da kusan shekaru hudu.

Tun a ranar Talata, ake bata kashi tsakanin kungiyar IS da ke Libiya da mayakan sa kai na cikin gida domin kwace ikon birnin Syrte.

A cewar kamfanin dillancin labaran Libiya na LANA, kungiyar IS da ke Libiya ta fille kan wasu mayakan goma sha biyu da ke adawa da ita, kuma ta rataye su lokacin da ake gumurzun kwace birnin Syrte. (Maman ADA)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China