in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Saudiya ta yi wa Iran gargadin da daina sanya hannu a cikin harkokin gida na sauran kasashen duniya
2016-01-10 13:59:28 cri
A jiya Asabar 9 ga wata, ministan harkokin waje na Saudiya, Adel al-Jubeir ya yi gargadi ga Iran cewa, kasarsa za ta dauki karin matakai idan Iran ba za ta daina sanya hannu cikin harkokin gida na sauran kasashe ba.

A gun taron manema labaru da aka shirya a Riyadh, mista Adel al-Jubeir ya furta cewa, dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu ta tsananta dalilin kasar Iran, a maimakon Saudiyya ko sauran kasashen Larabawa dake yankin tekun Pasha ba. Idan Iran ta ci gaba da bin manufarta a yanzu, Saudiya za ta dauki karin matakai domin mai da martani.

Kwamitin hadin gwiwa tsakanin kasashen Larabawa a yankin tekun Pasha (GCC) ya kira taron ministoci cikin gaggawa a jiya a birnin Riyadh, inda aka yi shawarwari kan tsanantar dangantaka tsakaninsu da Iran da sauransu. Mahalarta taron suna goyon bayan matsayin da membobin kungiyar GCC suke dauka kan kasar Iran, tare da yin Allah wadai da masu zanga zangar Iran da suka kai hari kan ofishin jakadancin Saudiya a kasar.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China