in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afirka ta Tsakiya tana fatan bunkasa hadin gwiwa da Sin a fannoni daban daban
2014-09-05 11:08:10 cri
Shugabar rikon kwaryar kasar Afirka ta Tsakiya Catherine Samba-Panza ta bayyana cewa, tana fatan kasarta da kasar Sin za su karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu bisa fannoni daban daban, musamman ma a fannonin da suka hada da samar da wutar lantarki, ayyukan noma, samar da kayayyakin more rayuwa da kuma samar da isashen abinci.

Madam Panza ta kara da cewa, kasar Afirka ta Tsakiya tana son ci gaba da habaka dangantakar zumunci dake tsakaninta da kasar Sin, haka kuma, tana fatan kasar Sin za ta ci gaba da taimakawa kasar Afirka ta Tsakiya wajen sake gina kasar, inda ta ce, batun tsaro shi ne abin ya fi damun gwamantin kasar.

An sha fuskantar tashin hankali a kasar Afirka ta Tsakiya, inda a ran 23 ga watan Yuli na wannan shekara, bangarorin biyu da rikicin kasar ya shafa da suka hada da kungiyar anti-Balaka da kuma kungiyar da ke adawa da tsohuwar gwamantin kasar ta Seleka suka sanya hannu kan wata yarjejeniyar dakatar da rikice-rikice a birnin Brazzaville, don fara shawarwarin sulhu a duk fadin kasar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China