in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manzon musamman na MDD na share fagen kira taro tsakanin jam'iyyun Syria a ranar 25 ga watan Janairun badi
2015-12-27 13:57:33 cri
A jiya Asabar 26 ga wata, manzon musamman kan batun Syria na MDD, Staffan de Mistura ya bayyana cewa, yana share fagen kira taron yin shawarwari tsakanin jam'iyyun siyasa na kasar Syria a ranar 25 ga watan Janairu mai zuwa a Geneva.

A wannan rana, a Geneva, mista Mistura ya ba da sanarwar cewa, a ranar 18 ga wata, kwamitin sulhu ya zartas da kudurin daidaita batun Syria ta hanyar siyasa, daga bisani, ya gaggauta kokarinsa na shiga tsakani kan batun Syria. Yana fatan kammala aikin yin shawarwari tare da jam'iyyun Syria a farkon watan Janairu na badi, daga bisani, za a kira taron yin shawarwarin wanzar da zaman lafiya tsakaninsu a ranar 25 ga watan Janairu mai zuwa a Geneva.

Ban da haka, mista Misturaya ya kalubalanci jam'iyyun kasar daban daban da su yi hadin gwiwa, su kawar da bambanci dake tsakaninsu domin kawo karshen wahalhalu da fararen hula suke sha. Dadin dadawa, ya yi kira ga kauracewa ayyukan da za su iya kawo cikas ga yunkurin siyasa, kuma ya yi kira ga kasa da kasa da su ci gaba da ba da taimako ga kasar Syria kamar yadda suke a yanzu.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China