in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya gana da zaunannun wakilan kwamitin sulhu na MDD, kan batun amfani da makamai masu guba a Syria
2013-08-31 17:11:42 cri
A ranar Juma'a 30 ga watan nan ne babban sakataren MDD Ban Ki-moon, ya gana da manyan wakilai na kasashe guda biyar na zaunannun membobin kwamitin zartaswar kwamitin sulhu na MDD, a hedkwatar majalissar dake birnin New York, don tattauna batutuwan da suka shafi yiwuwar amfani da makamai masu guba a kasar Siriya.

Kakakin babban sakataren MDD Martin Nesirky ya bayyana hakan. Ya ce Mr. Ban ya gaggauta kammala ziyarar kasashen ketare, don sauraron sabon rahoto game da binciken da aka yi, don gane da zargin amfani da makamai masu guba a kasar Syria.

Ya zuwa yanzu, tawagar masu bincike kan wannan batu ta MDD ta riga ta kammala ayyukanta, kuma za ta tashi daga birnin Damascus a yau Asabar 31 ga wata. Kakakin babban sakataren MDD ya kuma jadadda cewa, za a tsaida shawara kan wannan batun bayan kammala cikakken nazari kan samfurin sinadarai da tawagar binciken ta samo a kasar ta Siriya.

Bugu da kari, bisa labarin da aka samu a ran Juma'a 30 ga wata, babbar wakiliya mai kula da harkokin soja ta MDD Angela Kane, ta tashi daga kasar Syria zuwa Turkiya. A kuma ran 29 ga wata, kakakin mataimakin babban sakataren MDD ya bayyana cewa, hakan ba shi da nasaba da rade-radin da ake yi cewa kila kasashen yammacin Turai za su yi kawancen daukar matakan soja kan gwamnatin ta Siriya. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China