in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu na MDD da kungiyar adawar kasar Syria sun yi shawarwari a karo na farko
2013-07-28 16:59:35 cri
A ranar 26 ga wata a birnin New York na kasar Amurka, kwamitin sulhu na MDD da tawagar kungiyar 'yan adawar kasar Sham sun yi kwarya-kwaryar shawarwari a karo na farko, inda sabon shugaban kawacen kungiyar Ahmed Jarba ya halarci shawarwarin. Batutuwan biyu da aka tattauna a shawarwarin su ne tsaida kuduri game da batun mukamin shugaban kasar Bashar al-Assad da kuma gudanar da taron kasa da kasa kan batun kasar ta Sham wato taron Geneva.

Kungiyar 'yan adawa ta kasar Sham da masu goyon bayanta sun bayyana cewa, tilas ne shugaba Assad ya sauka daga mukaminsa, kana bai kamata a baiwa masu goyon bayansa mukami a hukumomin gudanarwa na wucin gadi na kasar ba. Har ila yau Jarba ya yi kira ga kasashen duniya da su kara matsin lamba ga shugaba Assad don tursasa shi amincewa da shirin warware rikicin kasar ta hanyar siyasa. Amma zaunannen wakilin kasar Rasha dake MDD Vitaly Churkin ya bayyana cewa, sanya wannan bukatu cikin sharadin gudanar taron na Geneva, zai kara shigar da shirin cikin mawuyacin hali. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China