in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawagar Babban kungiyar adawa ta Sudan ta kudu ta isa Juba
2015-12-22 10:39:12 cri
Tawagar babban kungiyar adawa na kasar Sudan ta kudu ta isa birnin Juba a ranar litinin din nan don tattaunawa da gwamnatin Shugaba Salva Kiir Mayardit a kan aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiya da bangarorin biyu suka rattaba ma hannu.

Kamar yadda kafar watsa labaran kasar ta bayyana, tawagar ta bar gabashin kasar inda take da rinjaye zuwa kasar Habasha kafin ta isa zuwa birnin Juba, sai dai an ce tawagar bata kunshi Shugaban ta ba Reik Machar.

A wani bangaren kuma radiyon MDD ta bada rahoton cewa kakakin Shugaban kasar Ateny Wek ya bayyana cewar bangarorin biyu za su zama abokan zaman lafiya ba abokan yaki ba.

Ya kara da cewar al'ummar kasar ta Sudan ta Kudu zasu fahimci cewar zaman lafiya ya samu , wanda wani sabon mafari ne a kasar.

Tawagar 'yan tawayen dai ya kamata su isa birnin Juba tun makonni 4 da suka gabata domin fara aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiyar da kuma shirin gwamnatin wucin gadi kamar yadda aka tsara a cikin yarjejeniyar amma cigaba da arangama tsakanin bangarorin biyu ya kawo tsaiko.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China