in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wang Min ya yi kira da a kare iko da moriyar mata a yankunan dake fama da rikice-rikice
2015-12-17 17:03:24 cri
A jiya Laraba 16 ga watan nan ne mataimakin zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Wang Min, ya yi kira ga kasashen duniya, da su yi hadin gwiwa, wajen bada kariya ga moriyar mata, da ta yara kanana a yankunan dake fama da tashe-tashen hankula.

Mr. Wang Min ya gabatar da wannan kira ne yayin da yake jawabi ga taron kwamitin sulhu game da batun fataucin mutane a yankunan dake fama da rikice-rikice. Ya ce a cikin 'yan shekarun da suka wuce, kungiyar IS da ta Boko Haram, da makamantan su, sun aikata laifukan kamawa da sayar da mutane a yankin Gabas ta Tsakiya da nahiyar Afirka da ma sauran wurare. Hakan a cewar sa ya haifar da babbar illa ga iko da moriyar mata da ta yara, tare da lalata yanayin zaman rayuwarsu.

A sabili da haka, Mr. Wang ya ce kamata ya yi kasashen duniya su yi hadin gwiwa tsakaninsu, domin ba da kariya ga iko da moriyar wannan rukuni na al'umma, a yankunan dake fama da rikice-rikice a duniya. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China