in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin na taka muhimmiyar rawa wajen hada kan kasahe masu tasowa, inji MDD
2015-10-08 10:14:27 cri
Mahalarta taron MDD kan batun cinikayya da samar da cigaba wato UNCTAD a takaice, sun bayyana cewar, kasar Sin tana bada gagarumar gudunmowa wajen hada kan kasashe masu tasowa saboda da yadda ta ke samar musu muhimman ababan more rayuwa.

Daraktan UNCTAD mai kula da kasashen Afrika masu tasowa Tesfachew Taffere, ya furta hakan a hirarsa da kamfanin dillancin labaran kasar Sin Xinhua, ya ce kasar Sin ta giggina muhimman ababan more rayuwa a kasashe masu tasaowa musamman a fannonin makamashi da sufuri.

Ya ce samar da ababan more rayuwar zasu taimaka wajen habaka cigaban tattalin arziki da kasuwanci a kasashen masu tasowa.

Mista Tesfachew, ya yabawa kasar Sin wajen tallafawa kasashen duniya da dama wajen yakar talauci da samar da ayyukan yi ga miliyoyin al'umma.

Idan za'a iya tunawa, a yayin gudanar da babban taron MDD kan batun cigaban kasashen duniya wanda aka gudanar a watan jiya a birnin New York, shugaba Xi Jimping na kasar Sin, ya yi alkawarin bada tallafin kudi kimanin dalar Amurka biliyan biyu domin aiwatar da shirin raya cigaban kasashe masu tasowa nan da shekara ta 2030. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China