in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Afrika na taimakawa juna karkashin tsarin hadin gwiwar kasashe masu tasowa
2015-12-16 21:00:16 cri
Ministan kasuwancin kasar Sin Mr. Gao Hucheng, ya shedawa manema labaru a yau Laraba cewa, Sin na baiwa kasashen Afrika tallafi bisa ka'idar daidaito da cimma moriyar juna, kuma hadin gwiwa tsakanin Sin da Afrika, mataki ne da bangarorin biyu ke dauka domin taimakawa juna, karkashin tsarin hadin kan kasashe masu tasowa.

Mr. Gao ya bayyana hakan ne yayin da ake gudanar da taron ministoci karo na 10 na kungiyar cinikayya ta duniya wato WTO a kasar Kenya. Ya ce Sin na turawa kasashen Afrika kwararru da masana domin bada tallafi, tana kuma hadin gwiwa da kasashen nahiyar a fannoni da dama, ciki hadda fannin bunkasa masana'antu. Sauran sassan sun hada da aikin gona, da kawar da talauci, da kiwon lafiya da dai sauransu, musamman a fannin ba da jiyya, matakin da ya sami yabo matuka daga jami'ai da jama'ar kasashen na Afrika.

Idan ba a manta ba, shugaban kasar Sin Mista Xi Jinping ya gabatar da ra'ayinsa na "Manyan ginshikai biyar" da "Shirin hadin gwiwa a manyan fannoni goma" a taron koli na dandalin tattaunawar hadin kai tsakanin Sin da Afrika, wanda ya gabata a farkon wannan wata da muke ciki a birnin Johannesburg, inda kuma Mista Xi ya yi alkawarin samar da tallafin kudi har dala biliyan 60. Game da hakan, Mista Gao ya ce Sin ta samar da wadannan tallafi ne bayan wasu kasashe dake karbar tallafi sun yarda da samu goyi bayan manufofin, kuma za su shiga cikin wannan aiki.

Ya ce Hanyar da Sin da kasashen Afrika za su bi nan gaba dangane da hadin gwiwar su, za ta hanzarta bunkasuwar tattalin arzikin kasar Sin har ma dukkanin nahiyar Afrika baki daya. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China