in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hadin gwiwar Sin da Afirka zai amfana wajen kyautata yanayin Afirka ta fuskar kiwon lafiya, in ji WHO
2015-12-06 11:11:26 cri

A yayin da aka gudanar da taron koli na Johanneburg na dandalin tattaunawar hadin gwiwa a tsakanin kasashen Sin da Afirka, Margaret Chen, babbar darektar hukumar kiwon lafiya ta duniya WHO ta halarci wani taron yin rigakafin cutar AIDS cikin hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka a birnin, inda a cewarta, shirye-shiryen hada kan Sin da Afirka za su taimaka wajen kyautata yanayin kasashen Afirka na ba da magani da kiwon lafiya.

Madam Chen ta ce, a yayin taron kolin, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya sake jaddada kasancewar harsashi mai inganci a tsakanin Sin da Afirka ta fuskar yin hadin gwiwa, tare da sanar da shirye-shirye guda 10 na yin hadin gwiwa a tsakaninsu cikin shekaru 3 masu zuwa, ciki har da taimakawa kasashen Afirka wajen kyautata yanayin ba da magani da tsarin kiwon lafiya. Hukumarmu ta WHO ta yaba wa hakan. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China