in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yin kokari cikin hadin gwiwar Sin da Afirka domin samun makoma mai kyau
2015-12-06 11:08:05 cri

Jaridar People Daily ta kasar Sin ta ba da sharhi yau Lahadi 6 ga wata, mai taken "bude sabon shafi cikin hadin gwiwar kasashen Sin da Afirka, a kokarin samun ci gaba tare".

Sharhin ya ce, gudanar da taron koli na Johannesburg na dandalin tattaunawar hadin gwiwa a tsakanin kasashen Sin da Afirka, ya dace da moriyar dukkan kasashen Afirka da Sin, sa'an nan ya cimma burinsu duka.

Taron koli na Johannesburg, taron koli ne na biyu a tarihin huldar da ke tsakanin kasashen Afirka da Sin, haka kuma karo na farko da aka gudanar da taron koli a nahiyar Afirka, wanda ya taka muhimmiyar rawa wajen inganta hada kan Sin da Afirka da kuma tsara manufar raya huldar da ke tsakanin sassan biyu a nan gaba.

Taron kolin ya kara azama kan raya Sin da Afirka tare bisa manyan tsare-tsare, inganta hadin gwiwarsu, kyautata samun moriyar bai daya na Sin da Afirka, da karfafa hada kan kasashe masu tasowa.

Yanzu an fara raya huldar abokantaka da hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka daga dukkan fannoni. Kasar Sin na son hada kai da 'yan uwanta na Afirka wajen yin kokari tare a fannin bude sabon shafi cikin hadin gwiwa, a kokarin samun ci gaba tare. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China