in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping da Jacob Zuma sun ba da jagoranci kan cikakken zaman taron FOCAC
2015-12-06 09:47:37 cri

Jiya Asabar 5 ga wata, an yi cikakken zaman taron shugabannin dandalin tattaunawar hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka(FOCAC) a birnin Johannesburg na kasar Afirka ta Kudu, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na kasar Afirka ta Kudu Jacob Zuma suka ba da jagoranci kan gudanarwar taron cikin hadin gwiwa. Haka kuma, wakilan FOCAC guda 52 da suka hada da wasu shugabannin kasashe 42, shugabar kungiyar tarayyar kasashen Afirka Nkosazana Dlamini-Zuma da sauransu sun halarci wannan taro.

Kaza lika, a yayin taron, an zartas da sanarwar taron kolin Johannesburg na FOCAC da kuma shirin Johannesburg daga shekarar 2016 zuwa shekarar 2018 na FOCAC bisa jagorancin da shugaba Xi Jinping ya bayar, inda kuma ya ba da jawabin rufe taron.

A yayin da yake jawabin rufe taron, shugaban kasar Afirka ta Kudu Jacob Zuma ya bayyana cewa, yana godiya matuka ga babbar gudummawar shugaban kasar Sin Xi Jinping, har ma da bangarorin kasar Sin baki daya suka samar wajen gudanarwar taron koli na wannan karo, kana, shugabannin kasashen Afirka da suka halarci taron sun nuna himma da kwazo ta aniyarsu wajen zurfafa hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka, sa'an nan, ko shakka babu, ra'ayoyin da aka cimma kan batutuwa da dama a yayin taron za su ciyar da bunkasuwar dangantakar dake tsakanin Sin da Afirka gaba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China