in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya bukaci a gaggauta hadin gwiwwa da kasar Masar a bangaren samar da kayayyaki  da tsaro
2015-12-05 13:15:54 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bukaci a gaggauta hadin gwiwwa a bangaren samar da kayayyaki da tsaro da kasar Masar.

A ganawar da ya yi da Firaministan kasar ta Masar Sherif Ismaila a ranar jumma'an nan a gyefen wajen taron FOCAC a birnin Johannesburg na kasar Afrika ta kudu, Shugaba shugaba Xi ya ce ya kamata a bunkasa manyan ayyukan samar da kayayyaki a bangaren lantarki, sufuri da gina ababen more rayuwa a karkashin shirin ziri daya hanya daya.

Ya ce, kasar Sin za ta ci gaba da goyon bayan shirin kasar Masar na samar da zaman lafiya da cigaba kuma a shirye take ta hada kai da kasar Masar don daga matsayin hadin gwiwwar dake tsakaninbangarorin biyu bisa manyan tsare-tsare gaba..

A nasa bangaren, Firaministan firaministan kasar Masar Sherif Ismail ya yaba matuka da jawabin da Shugaba shugaba Xi Jinping ya gabatar a bikin bude taron na FOCAC, inda ya ce jawabin zai kara haifar da sakamako mai kyau kan gwiwa tsakanin Sin da Afrika.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China