in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin: Taron koli na FOCAC zai bude wani sabon babi na raya dangantaka tsakanin Sin da kasashen Afirka a fannonin tattalin arziki da cinikayya
2015-12-02 19:34:15 cri
A yau Laraba 2 ga wata ne kakakin ma'aikatar kasuwancin kasar Sin Shen Danyang, ya bayyanawa wani taron manema labaru cewa, a yayin taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka na FOCAC, wanda za a bude a kasar Afirka ta Kudu, za a gabatar da jerin sabbin sahihan matakan hadin gwiwa, wadanda za su bude wani sabon babi na raya dangantaka tsakanin Sin da kasashen Afirka a fannonin tattalin arziki da cinikayya.

Mr. Shen ya ce sabbin matakan za su kunshi abubuwa iri iri, wadanda za su bayyana sabbin alamun hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu, da biyan bukatunsu a fannin tsarin bunkasuwa, da hadin gwiwa tsakaninsu, tare da samun fasahohi da nasarori tare.

Game da jita jitar da wasu suke yadawa a Afirka, cewa wai Sin na barazana ga nahiyar, kuma abin da take yi a Afirka mulkin mallaka ne na sabon salo, da kuma tababar da ake yi game da manufar hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka, Mr. Shen Danyang ya bayyana cewa, ana nuna tababar ne ba tare da la'akari da hakikanin abubuwan dake abkuwa ba, ba kuma tare da duba hakikanin yanayin da ake ciki a fannin dangantakar Sin da kasashen na Afirka ba. Ya ce tun asali, kasar Sin aminiyar nahiyar Afirka ce, hakan kuma zai ci gaba da dorewa nan gaba da ma ko da yaushe. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China