in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan ta'adda na shirin kaiwa ofishin jakadancin Amurka da ke Afirka ta Kudu hari
2015-09-09 11:20:18 cri
Ofishin jakadancin Amurka da ke kasar Afirka ta Kudu ya bayyana cewa, ya samu bayanan sirri da ke nuna alamun cewa, masu tsattsauran ra'ayi na shirin kai masa hari.

Wata sanarwa da ofishin jakadancin ya fitar ta bayyana cewa, sauran wuraren da 'yan ta'addan ke shirin kai harin sun hada da gine-ginen gwamnatin Amurkar da sauran wuraren da ke da alaka da harkokin kasuwancin Amurka. Sai dai sanarwar ba ta yi wani karin haske game da lokaci ko takamaimai wuraren da aka tsara kai wadannan hare-haren ba.

Don haka, ofishin jakadancin na Amurka ke shawartar jama'a da su sanya ido sosai a wuraren da ke kewaye da su, kana su rika bibiyar kafofin watsa labarai don karin bayani tare da bin umarnin hukumomi.

Ofishin jakadancin na Amurka ya dauki wannan mataki ne sakamakon harin ta'addanacin da aka kai rukunin shagunan zamanin nan na West Gate a birnin Nairobin kasar Kenya, harin da ake zargin 'yar kasar birtaniya mai suna Samantha Lewthwaite da kitsa shi, bayan da aka ganta tana leken asiri a rukunin ofisoshin jakandancin kasashen waje da ke kasar Afirka ta Kudu kafin kai harin.

Bayanai na nuna cewa, Samantha wadda yanzu haka ke amfani da Natalie Faye Webb, tana Afirka ta Kudu tsakanin shekarar 2008 zuwa 2011, kuma tana tafiye-tafiye da fasfon kasar Afirka ta kudu.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China