in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhun MDD ya zartas da kudurin kara karfin yaki da kungiyar IS
2015-11-21 13:20:01 cri
A jiya Jumma'a 20 ga wata, kwamitin sulhu na MDD ya zartas da wani kuduri, inda aka tattauna kan harin ta'addancin da kungiyar IS ta yi, inda ake ganin cewa, kungiyar ta zama mai barazana ga tabbatar da zaman lafiya da tsaro na duniya da ba a taba ganin irinsa ba, shi ya sa, kwamitin sulhu ya yi kira ga kasashen duniya da su kara karfin yaki da kungiyar IS.

Kwamitin sulhu ya kalubalanci kasashe membobin MDD masu karfi da su dauki kowane irin matakai a wuraren na Syria da Iraki dake hannun kungiyar IS, su yi hadin gwiwa domin yin rigakafi da yaki da kungiyoyin ta'addanci, kamarsu kungiyar IS, da ta Al-Qaeda da sauransu, domin rushe sansanoninsu a wadannan kasashen biyu.

A jiya kuma ma'aikatar harkokin waje ta Rasha ta ba da sanarwar cewa, ministan harkokin waje na Rasha Sergei Viktorovich Lavrov ya buga waya da sakataren harkokin waje na Amurka John Kerry a wannan rana, inda suka yi shawarwari kan yadda za su shawo kan matsalar kungiyar IS, da sa kaimi ga gwamnatin Syria da ta yi shawarwari da jam'iyyun adawa da gwamnati da sauransu. Ban da haka, bangarorin biyu sun yi shawarwari kan yadda za a tabbatar da sakamakon da aka samu a gun taron ministocin harkokin waje kan batun Syria a Vienna sau biyu. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China