in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar IS ta ce, ta kashe wani Basine da wani dan kasar Norway da ta yi garkuwa da su
2015-11-19 10:16:54 cri
Kungiyar da ke da'awar kafa daular Musulunci ta IS ta furta a jiya Laraba cewa, ta kashe wani Basine da wani dan kasar Norway da ta yi garkuwa da su.

A wannan rana, mujallar Dabiq karkashin shugabancin kungiyar IS ta wallafa hotuna kan yadda kungiyar ta harbe kawunan wadannan mutane biyu da bindiga, har suka mutu, amma kungiyar ba ta fayyace sunayen mutanen biyu ba.

Tun da farko dai kungiyar IS ta yi shelar cewa, tana garkuwa da wani Basine dan asalin birnin Beijing mai sunan Fan Jinghui da wani dan kasar Norway mai suna Ole Johan Grimsgaard-Ofstad.

A yau ne, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei ya ce, Sin ta lura da wadannan labaru, wadanda suka girgiza ta matuka, za ta ci gaba da tabbatar da sahihancin wadannan bayanai

A cewar kakakin, tun bayan da aka yi garkuwa da Basinen, gwamnatin Sin ke iyakacin kokarin ganin an ceton shi.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China