in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta nuna goyon bayan ta ga Rasha game da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali
2015-11-18 20:39:01 cri
Mahukunta a Rasha sun tabbatar da cewa harin ta'addanci ne ya sabbaba hadarin jirgin saman kasar a ranar 31 ga watan Oktoba. Game da wannan batu, kakakin ma'aikatar harkokin waje ta Sin, Hong Lei ya bayyana cewa kasar Sin na matukar goyon bayan Rasha, a yunkurin da take yi na tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, da kuma daukar matakan yaki da ta'addanci. Dadin dadawa, Sin na fatan tabbatar yanayin zaman lafiya da kwanciyar hankali a Rasha da ma dukkanin sauran kasashen duniya baki daya.

A gun taron manema labaru da aka shirya a yau Laraba, mista Hong ya bayyana cewa ta'addanci abokin gaba ne ga dukkanin bil'adama. Don haka a koda yaushe Sin ke nuna kiyayyar ta ga kowane irin nau'in aiki na ta'addanci. Har ila yau a matsayin ta na aminiyar hadin gwiwa a duk fannoni kuma bisa manyan tsare tsare, Sin tana goyon bayan Rasha, wajen tabbatar da tsaro, da zaman lafiya a yankunan ta, da ma duk wasu matakai na yaki da ta'addanci da Rashan za ta aiwatar.

Mr. Hong ya ce Sin na fatan karfafa hadin gwiwa tsakaninta da Rasha, da ma dukkanin sauran kasashen duniya a fannin tsaro, da zummar shawo kan barazanar ta'addanci, da kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China